An Kaddamar da Ƙungiyar Matasan Mata Ƙwararru a Fannin Watsa Labarai a Bauchi

Mar 14, 2026 - 19:09
 0  10
An Kaddamar da Ƙungiyar Matasan Mata Ƙwararru a Fannin Watsa Labarai a Bauchi

An kaddamar da Ƙungiyar Matasan Mata Ƙwararru a Fannin Watsa Labarai (YFPM) a Jihar Bauchi State, domin ƙarfafa matasan ‘yan jarida mata tare da inganta ƙwarewarsu a harkar watsa labarai.

Da take jawabi yayin taron kaddamarwar, shugabar YFPM ta jihar Bauchi, Aishatu Abdullahi Muhammad, ta bayyana ƙaddamar da ƙungiyar a matsayin wani muhimmin mataki na samar da dandalin da zai tallafa tare da ƙarfafa matasan ‘yan jarida mata ta hanyar horaswa, shawarwari da kuma haɗin gwiwa tsakanin ƙwararru a fannin aikin jarida.

Ita ma wacce ta kafa ƙungiyar kuma shugabar ta a matakin ƙasa, Maryam Usman Nagado, ta ce an kirkiro ƙungiyar ne domin samar da sabuwar ƙarni na ƙwararrun ‘yan jarida mata masu gaskiya, ƙwarewa da jajircewa wajen gudanar da aikinsu.

Ta ƙara da cewa manyan manufofin ƙungiyar sun haɗa da inganta aikin jarida mai cike da gaskiya da rikon amana, samar da shirye-shiryen horaswa da jagoranci ga matasa mata a kafafen yaɗa labarai, ƙarfafa haɗin gwiwar ƙwararru, da kuma amfani da kafafen watsa labarai wajen kawo sauyi mai kyau a cikin al’umma.

A jawabansu daban-daban, Nafisa Adamu Muhammad daga Sa'adu Zungur University da kuma shugaban Nigeria Union of Journalists (NUJ) reshen Bauchi, Umar Sa’idu, sun jaddada muhimmancin ƙwarewa, bin ƙa’idojin aikin jarida da kuma amfani da harsunan gida wajen isar da saƙonni a kafafen watsa labarai.

Sun kuma bayyana irin rawar da mata ke takawa wajen tsara muhawara da tattaunawa a cikin al’umma, tare da ƙarfafa su da su ci gaba da taka rawa a fannin yaɗa labarai.

Tun da farko a jawabinsa, kwamishinan yaɗa labarai da sadarwa na jihar Bauchi, Usman Shehu Usman, ya yabawa wannan shiri, yana mai cewa mataki ne mai kyau wajen ƙarfafa aikin jarida a jihar.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta bai wa ƙungiyar goyon baya, ciki har da samar da ofishi da kuma taimako a fannin fasaha domin sauƙaƙa gudanar da ayyukanta.

Bayan kaddamarwar, an bayyana sabbin shugabannin reshen YFPM na jihar Bauchi inda Aishatu Abdullahi Muhammad ta zama shugaba, yayin da Rafee’ah Muhammad ta zama mataimakiyar shugaba.

Sauran shugabannin sun haɗa da Hajara Shaibu Dankama a matsayin sakatare, da kuma Khadija Ahmed Salihu a matsayin mataimakiyar sakatare, tare da sauran mambobi da za su jagoranci ayyukan ƙungiyar a jihar.

What's Your Reaction?

Like Like 0
Dislike Dislike 0
Love Love 0
Funny Funny 0
Angry Angry 0
Sad Sad 0
Wow Wow 0