Sojoji Sun Dakile Yunkurin Sace Jama’a, Sun Ceto Mutane 157 a Borno
Daga Orbit News 24 | 31 ga Maris, 2026
Sojojin rundunar Operation HADIN KAI sun yi nasarar dakile wani yunkurin sace jama’a da mayakan Boko Haram/ISWAP suka kai, inda suka ceto mutane 157 a kan hanyar Buratai–Kamuya a Jihar Borno.
A cewar majiyoyin tsaro, lamarin ya faru ne lokacin da ‘yan ta’addan suka kai hari kan motocin da ke dauke da fararen hula a kan hanyar, inda suka yi yunkurin kwashe mutanen zuwa cikin daji ta amfani da kusan motoci 17.
Sojojin da ke rakiya ga fararen hular sun yi gaggawar mayar da martani tare da fafatawa da maharan, yayin da aka tura rundunar gaggawa (Quick Reaction Force) domin karfafa aikin.
Daga bisani, matsin lambar da sojojin suka yi ya tilasta wa ‘yan ta’addan janyewa zuwa yankin Mangari.
Dukkan mutanen da aka sace an kubutar da su cikin koshin lafiya, kuma an kai su wurare masu tsaro.
Sai dai, an samu raunuka a bangaren sojoji, inda sojoji biyar suka jikkata sakamakon fashewar bam (IED) yayin da suke bin ‘yan ta’addan da suka tsere. A halin yanzu suna karbar kulawar likitoci.
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa har yanzu sojoji na cikin shirin ko-ta-kwana a yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan tsabtace wurare domin hana sake faruwar hare-hare.
Wannan nasara na daga cikin kokarin da ake ci gaba da yi wajen yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.
What's Your Reaction?
Like
0
Dislike
0
Love
0
Funny
0
Angry
0
Sad
0
Wow
0